in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran da IAEA sun cimma matsaya daya kan wasu fannonin dake cikin shirin binciken nukiliya
2013-02-14 16:35:17 cri
Kamfanin dillancin labaru na Fars na kasar Iran ya ba da labari a ranar Laraba 13 ga wata cewa, Iran da hukumar makamashin nukiliya ta IAEA sun kammala shawarwari na yini guda, inda bangarorin 2 suka cimma matsaya daya kan wasu fannonin dake cikin shirin binciken nukiliya da ake neman yi wa kasar Iran, sannan suka amince da ci gaba da tattaunawa a tsakaninsu.

Kamfanin Fars ya ruwaito wakilin Iran dake hukumar IAEA Ali Asghar Soltanieh yana mai cewa, bangarorin 2 sun kau da wasu daga cikin sabanin ra'ayin dake tsakaninsu, har ma sun cimma matsaya daya kan wasu fannoni masu muhimmanci, kana za su kara kira taron don tattauna shawarwarin da aka gabatar a wannan karo. Sai dai ba'a bayyana fannonin da akacimma ma matsaya a kai ba, balle ma lokaci da wurin da za a kira taron mai zuwa.

Kafin haka dai, hukumar IAEA da Iran sun riga sun yi shawarwari sau da dama don tabbatar da shirin binciken nukiliya. A taron da ya gabata da aka kira a tsakiyar watan Janairun bana, an kasa samun wani ci gaba mai gamsarwa. Hakan yasa hukumar IAEA ta kasa samun damar shiga sansanin Parchin na kasar Iran don gudanar da bincike.

Ban da haka, kasar Iran da sauran kasashe 6 masu ruwa da tsaki a cikin batun nukiliyar kasar, wato su Amurka, Birtaniya, Faransa, Rasha, Sin da Jamus, za su yi taro a Alama-Ata na kasar Khazakstan a ranar 26 ga watan da muke ciki.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China