in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar soji a Nigeria za ta bukaci kafa kotun musamman domin shari'ar 'yan kungiyar Boko Haram
2013-02-10 16:30:26 cri
Mataimakin darakta mai lura da sashen harkokin da suka shafi farar hula a ma'aikatar tsaron Nigeria, Air-Kwamanda Ademola Onitiju, ya bayyana aniyar rundunar sojin kasar, ta gabatar da bukatar ta ga mahukuntan kasar, domin kafa wata kotun musamman, da zata gudanar da shari'ar mambobin kungiyar nan ta Boko Haram, wadanda rundunar ta cafke a sassan kasar daban-daban.

Onitiju ya bayyana hakan ne ga manema labaru ranar Asabar 9 ga watan nan a garin Maiduguri babban birnin jihar Borno, yana mai cewa rundunar sojin zata kafa wani kwakkwaran kwamitin bincike, da zai nazarci zargin da ake wa wadanda rundunar ke tsare da su, don gane da kai hare-hare, da kisan mutane a yankunan kasar daban-daban.

Mataimakin daraktan yace tawagar rundunar ta ziyarci garin Maiduguri ne, domin saduwa da dukkanin masu ruwa da tsaki, dama shuwagabannin al'umma, da nufin karfafa dangantaka, da neman hadin kan su, ga bukatar sake maido da kyakkyawan yanayin zamantakewa a jihar, dama ragowar yankunan dake arewacin kasar.

Daga nan sai ya musanta zargin da akewa jami'an rundunar, na kashe wasu daga manbobin kungiyar ta Boko Haram, yana mai cewa dakarun soji, na aiki ne domin dawo da managarcin yanayin zaman lafiya, bawai kisan farar hula ba. (Saminu Alhassan Usman)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China