in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta tanadi shirin aikin taimakawa bil Adama a Congo(Kinshasa)
2013-02-08 11:30:11 cri
Ofishin gudanar da harkokin ayyukan jin kai na MDD wato OCHA ya sanar a ranar Alhamis 7 ga wata da cewa, cibiyoyin ba da agaji na MDD da abokan huldarsu sun bullo da wani shirin ba da agaji ga bil Adama a ranar Alhamis a birnin Kinshasa, babban birnin kasar jamhuriyyar dimokradiyyar Congo DRC.

Shirin wanda ya tanadi kudade da yawansu ya kai dalar Amurka miliyan 892.6 ya cimma bukatun mutane miliyan 3.9 a fadin kasar, wadanda suke fama da karancin abinci, cututtuka da yake-yake a wannan shekara, in ji sanarwar.

An bayyana cewa, kudaden za su taimaka wajen samar da tallafi a fannonin abinci, wuraren kwana, kariya da kuma shirin samar da ruwa da tsabtace muhalli don kare jama'a daga cututtukan dake da hadari ga rayuka kamar cholera da bakon dauro.

Shirin har wa yau na mai burin taimakawa mahukunta su inganta ayyukan amfanin jama'a har ma da ilmi. (Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China