in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNESCO ta jaddada alkawarinta na kiyaye kayayyakin tarihin kasar Mali
2013-02-03 16:43:52 cri
Hukumar kula da harkokin ilimi, kimiyya da fasaha, da al'adu ta MDD (UNESCO), ta ba da sanarwa a ranar Asabar 2 ga wata cewa, babban darektan hukumar Madam Irina Bokova, da ke ziyara a kasar Mali, ta sake jaddada alkawarin da kungiyarta ta yi na kokarin kiyaye, da sake gina kayayyakin tarihin kasar ta Mali.

Sanarwar ta bayyana cewa, shugaban kasar Faransa Francois Hollande, tare da Madam Bokova sun kai ziyara a kasar Mali tare. Haka zalika sanarwar ta ce, daya daga dalilan ziyarar shi ne, kaddamar da aikin tantance yanayin da ake ciki a kasar ta Mali a fannin kiyaye kayayyakin tarihi, musamman bisa la'akari da yadda wutar yaki ke ruruwa a kasar, sa'an nan Madam Bokova za ta kaddamar da wani shiri tare da gwamnatin kasar, na wanzar da ayyukan hukumar ta UNESCO a Mali.

An ce, wannan ziyara za ta baiwa Madam Bokova damar tattaunawa da masu fada a ji na hukumomin Timbuktu da Bamako, kana za ta kaddamar da shirin kungiyarta na tallafawa don kare, da kuma sake gina kayayyakin tarihi na al'adu dake kasar ta Mali.

Yanzu dai kasar Malin na da manyan kayayyakin tarihi da al'adu 4, ciki hadda tsohon garin Timbuktu, da kabarin Askia dake garin Gao. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China