in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sudan ta zargi Sudan ta Kudu da yi wa jarjeniyoyin da aka cimma zagon kasa
2013-01-29 10:51:49 cri
Wasu rahotannin baya bayan nan na bayyana cewa, kasar Sudan na zargin makwafciyarta wato Sudan ta kudu, da yin zagon kasa ga yarjeniyoyin da aka cimma tsakanin shugabannin bangarorin biyu.

Yayin zantawar sa da manema labaru ranar Litinin a birnin Khartoum, jim kadan bayan halartar wata tattaunawa tsakanin bangarorin biyu, jagoran tawagar ta Sudan Idris Abdul-Ghader ya ce Sudan ta kudu ta yi watsi da batun killace yankin nan na "Mile 14", wanda bisa yarjejeniyar da kwamitin tsaron kungiyar AU ya jagoranta aka hana ko wane bangare jibge soji a yankin, tare da sanya tsaron sa, kan doron sharuddan da kasashen biyu suka amince da su.

Wannan dai yanki na "Mile 14" dake kan iyakar Gabashin Darfur ta Sudan, da kuma Sudan ta Kudu, na cikin muhimman yankunan da bangarorin biyu ke martabawa, kasancewar sa mai kyakkyawar kasar noma da dausayi.

Cikin watan Satumbar bara a birinin Addis Ababa na kasar Habasha ne dai, shugabannin kasashen biyu, suka rattaba hannu kan shawarwarin hadin gwiwa, da inganta tsaro, da kuma batutuwan da suka shafi warware matsaloli masu alaka da rabuwar su. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China