in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'an MDD da na Syria sun tattauna kan yadda za a samar da wuraren kwana ga 'yan gudun hijira
2013-01-28 15:26:00 cri
Ran 27 ga wata, mataimakiyar babban sakatare da ke kula da harkokin jin kai na MDD, kuma mai shiga tsakani kan gudanar da harkokin ba da taimakon gaggawa, Valerie Amos ta ziyarci babban birnin kasar Syria, Damascus, inda ta gana da ministan kwadago da kuma kula da harkokin zamantakewar al'ummar kasar ta Syria Jassim Zakaria, don tattaunawa kan yadda za a gudanar da ayyukan ba da agaji ga 'yan gudun hijira da kuma samar masu da wuraren kwana.

Bisa kididdiyar da MDD ta yi, an ce, a halin yanzu, akwai mutane miliyan 4 dake bukatar taimakon jin kai a kasar Syria, yayin da kuma wasu miliyan 2 sun rasa gidajensu.

Bayan ganawar tasu, Jassim Zakaria ya bayyana cewa, an sami sakamako mai gamsarwa. To amma bai bayyana cikakken shirye-shiryen da bangarorin biyu suka tsara ba.

Tuni a wannan rana, Valerie Amos ta ziyarci wani wurin da ake kwantar da 'yan gudun hijira da ke birnin Damascus, inda ta nuna cewa, ziyarar ta wannan karo, ta fi mai da hankali ne kan ayyukan wasu tasoshin kiwon lafiya.

Wannan shi ne karo na uku da ta kai ziyara a kasar Syria bayan da kasar ta fada cikin rikici tun shekarar 2011, tana kuma shirya ganawa tare da ministan harkokin wajen kasar Syria. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China