in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yar takarar mukamin shugabancin kungiyar WTO za ta baiwa kudurorin taron Doha fifiko
2013-01-27 16:49:26 cri
Daya daga 'yan takarar nahiyar Afirka dake neman mukamin shugabancin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, Amina Mohammed, tace muddin aka zabe ta, tofa la shakka za ta baiwa batun karkare batutuwan da aka tattauna yayin taron kungiyar na Doha cikakken muhimmanci.

Amina wadda 'yar asalin kasar Kenya ce, kuma kwararriyar ma'aikaciyar Diflomasiyya, ta shaidawa kamfanin dillancin labaru na kasar Sin Xinhua cewa, matakin kammala batutuwan da aka fara tattaunawa a taron na Doha, zaimakawa wajen samar da daidaito, da habakar tattalin arzikin kasashen duniya baki daya, baya ga samar da karin arziki da yalwa da tace hakan zai haifar.

Amina dake wannan tsokaci yayin da take halartar taron kungiyar AU karo na 20 dake gudana a birnin Addis Ababa na kasar Habasha, na burin samun karin goyon baya daga wakilan kasashen Afirka, dama na ragowar kasashen duniya dake halartar taron.

Muddin dai ta kai ga cimma nasarar samun wannan mukami, za ta kasance mace ta farko, muka 'yar Afirka ta daya da ta taba jagorantar kungiyar ta WTO.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China