in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kulaf din Super Eagle na Nigeria na kan shan wani garan bawul na shekaru 5, inji kocin kungiyar
2013-01-23 16:13:08 cri
Kocin kungiyar kwallon kafar Nigeria Stephen Keshi ya bayyanawa manema labaru cewa a yanzu haka kungiyar Super Eagles da yake jagoranta na kan hanyar zama wata kungiya mai nagarta, wadda zata zamo abun alfaharin masu kallo, muddin dai ta kammala shan garan fuskar da ya ce a yanzu haka ake yi mata. Keshi wanda ya bayyana hakan jim kadan kafin fara wasan kungiyar da takwararta ta Burkina Faso da yammacin ranar Litinin din data gabata a birnin Johanesburg, ya ma ce kulab din na Super Eagle ba wai zai mai da hankali ne kawai kan wasannin da zai buga a gasar cin kofin nahiyar Afirka ba ne kadai, a'a har ma da dukkanin tsare-tsaren da za su kawo masa nasara a nan gaba. Don haka koci Keshi ke cewa za su ci gaba da gudanar da manufofin daukaka matsayin kulaf din tsawon shekaru 5, inda ake sa ran ganin kwalliya ta biya kudin sabulu nan da shekara ta 2018.

Bugu da kari kocin Super Eagles din ya ce burin cimma wannan manufa ne ma ya sanya shi sanya 'yan wasa masu karancin shekaru cikin kungiyar a wannan karo, da ma rage yawan tsoffin 'yan wasa kamar dai yadda ake gani a jerin sunayen 'yan wasan da suke bugawa Nigeriar kwallo a gasar AFCON ta bana. Ko da yake dai wasu daga masu nazarin kungiyar sun yi mamakin rashin sanya 'yan wasa irin su Peter Odemwingie, da Obafemi Martins, cikin wadan da za a je da su gasar ta Afirka ta Kudu a bana.

Nigeriar dai na cikin kasashen da suka yi suna matuka a fagen taka leda, musamman ma a nahiyar Afirka, sai dai a baya-bayan nan ta sha fama da matsaloli da dama, ciki hadda gaza samun damar zuwa gasar cin kofin nahiyar da ya gabata. Lamarin da ya sanya 'yan kallo da masu sharhi sanya ido a wannan karo, domin ganin ko za ta sauya zani.

A hannu guda kuma wannan wata dama ce ga sabon kocin kungiyar wato Stephen Keshi, ta ya nunawa duniya irin kwarewar sa, da sanin makamar aiki, a matsayin sa na kocin gida, wanda kuma a baya ya taba bugawa kungiyar ta Super Eagles kwallo, yayin da kungiyar ta lashe wannan kofi na nahiyar Afirka a shekarar 1994, ta kuma taka rawar gani a gasar cin kofin duniya daya gudana a kasar Amurka. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China