in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar 'yan tawayen M23 ta zargi gwamnatin RDC-Congo da saka da warwara
2013-01-22 14:15:45 cri
Gungun 'yan tawayen M23 ya zargi gwamnatin Kinshasa da wani aikin saka da warwara na amicewa da yin shawarawari a kasar Uganda a yayin da kuma a lokaci guda take fatan ganin an tura sojojin kasa da kasa dubu hudu domin shiga tsakani in ji mista Stanislas Baleke, kakakin kungiyar M23 a cikin wata hirarsa da Xinhua kwanan nan.

Gwamnatin Congo tana cigaba da tattauna hanyar ganin a zuba sojojin kasa da kasa da su shiga tsakani a yankin Kivu in ji mista Baleke, sannan ya kara da cewa wadannan ayyukan alla wadai dake faruwa a daidai wannan lokaci da muke nuna niyyarmu ta warware wannnan rikici cikin ruwan sanyi.

A cewar kakakin M23, gwamnatin Kinshasa na neman kara samun lokaci kafin zuwan wadannan sojojin kasa da kasa dubu hudu, wadanda za a ba su nauyin sa ido a kan iyakar RDC-Congo da Rwanda da kuma farautar 'yan tawayen M23 dake gabashin kasar RDC-Congo.

Yan tawayen M23 sun amince da tsagaita bude wuta a ranar 8 ga watan Janairun da ya gabata a yankin Arewacin Kivu da kuma gabashin RDC-Congo. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China