in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Afrika ta Kudu zai yi amfani da damar taron Davos domin janyo hankalin masu zuba jari
2013-01-22 13:58:05 cri
Shugaban Afrika ta Kudu, Jacob Zuma zai yi amfani da taron tattalin arziki na Davos a kasar Switzerland domin janyo hankalin masu zuba jari ta fuskar tattalin arziki da masana'antu na duniya domin ayyukan gine gine a cikin kasar da ma Afrika baki daya.

Hakan zai taimaka wajen habakar tattalin arzikin nahiyar a cikin tsawon lokaci, in ji kakakin fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu, mista Mac Maharaj a kwanan nan.

Shugaba Zuma zai yi amfani da wannan dama a taron Davos domin yayata shirin cigaban kasa na Afrika ta Kudu (PDN) da ya kasance wani hangen babbar kasa da Afrika ta Kudu take kokarin zama nan da shekarar 2030 in ji mista Maharaj. Fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu ta yi wannan sanarwa kafin tashin shugaba Zuma zuwa Davos na Switzerland

A yayin taron, mista Zuma zai gayyaci kamfanonin kasa da kasa ga zuba jari a cikin ayyukan gine gine na biliyoyin kudin Rands da zai taimaka ga kawo sauyin tattalin arziki da na jama'a a kasar bayan kammala wannan taro. Shugaba Zuma na kare yankin bunkasar gine gine tsakanin Arewa da Kudu na AU dake tashi daga Durban zuwa Dar-es-Salaam, da kuma fatan yayata shi a taron Davos, a cewar kakakin fadar shugaban kasar Afrika ta Kudu. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China