in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu daga jama'ar Nijeriya sun nuna rashin jin dadi da rashin wutar lantarki a yayin wasan kwallon kafa na cin kofin Afirka da kulaf din kasar su ya buga
2013-01-22 11:19:16 cri
A ran 21 ga wata da yammaci bisa agogon wurin a yayin gasar kwallon kafa ta cin kofin Afirka dake gudana, kungiyar Super Eagle ta Nijeriya da ta Burkina Faso sun tashi canjaras wato ci daya da daya, amma a birnin Abuja, babban birnin tarayyar Nijeriya, wasu yankunan birnin ba su da wutar lantarki, wadda hukumar kula da samara da wutar lantarkin ke samarwa, sakamakon haka wasu jama'a masu kaunar kallon wasan kwallon kafan da ba su da injin janareto ba su samu damar kallon wasan ba.

Wakilinmu dake Abuja ya ce ya zanta da wasu mazauna birnin wadanda suka tabbatar da cewa, a tsakiyar ranar ta litinin har zuwa dare, babu wutar lantarki, amma bayan gasar cin kofin Afirkan da aka buga tsakanin kungiyar Nijeriya da Burkina Faso, an ba da wutar lantarki tad an wani lokaci , sa'an nan kuma aka sake daukewa. Wani mazaunin birnin na Abuja malam Bello, ya nuna rashin jin dadinsa, sabo da bai samu damar kallon wasan ba sabo da rashin wuta. Malam Bello ya ba da shawawra ga hukumar da ke samar da wutar da ta tabbatar da baiwa jama'a wutar yayin wasan, koda ba za a samu wutar a ragowar lokuta ba.

Danladi, wakilin CRI daga Abuja, Nijeriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China