A cewar shugaban hukumar lura da wasannin kwallon kafar kasar Namibia John Muinjo, kulaf din Zambia ya bayyana musu kurewar lokaci, a matsayin dalilin fasa buga wasan da a baya aka tsara gudanarwa ranar Talatar data gabata.
Zambia dai bata samu nasara a wasannin sada zumunci da tayi da kasashen Tanzania da Angola ba, ta kuma yi kunnen-doki da Morocco, za kuma ta buga wasan farko a rukunin C tare da kasar Habasha ranar 21 ga watan nan a Nelspruit. (Saminu Alhassan Usman)