in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar kiyaye muhallin Sin ta yi kira da a kiyaye ikon sanin yanayin muhalli na jama'ar kasar
2013-01-15 15:44:33 cri

Bisa nazarin da aka yi kan sakamakon bincike kan ingancin iska da kuma hasashen yanayi a kasar Sin, an ce, a halin yanzu, za a ci gaba da samun hazo mai tsanani a arewacin kasar, da kudancin kogin Yangtse da dai sauran yankunan tsakiya da gabashin kasar.

Wurare da yawa na fama da gurbacewar yanayi mai tsanani, dake janyo illa ga zaman rayuwar jama'ar Sin da ma lafiyar jikinsu.

Ran 14 ga wata, hukumar kula da harkokin kiyaye muhallin kasar ta Sin ya ba da wata sanarwa inda ta nuna cewa, a halin yanzu da jama'ar kasar suke fama da gurbacewar yanayi, kamata ya yi biranen kasar su mai da hankali kan ayyukan bincike ingancin iska yadda ya kamata.

Haka zalika sanarwar ta yi kira da a kara mai da hankali kan ayyukan kaucewar gurbacewar yanayi, da kuma dukufa wajen rage mugun tasirin da gurbacewar yanayi ta kawo wa jama'a, ta yadda za'a kiyaye lafiyar jama'ar kasar. Sanarwa ta kara da cewa, kamata ya yi a watsa labarai cikin lokaci kan ingancin iska ga al'ummomin kasar ta kafofin watsa labarai iri-iri, kamar su gidajen rediyo, shirye-shiryen talabijin, shafin intanet, da kuma jaridu da dai sauransu, ta yadda za a iya kiyaye ikon samar da bayanai kan yanayin muhalli ga jama'ar kasar.

Daga bisani kuma, hukumar kula da harkokin kiyaye muhallin kasar ta Sin ta bukaci a mai da hankali kan kananan abubuwa cikin iska dake gurbata muhalli, da kuma dukufa kan ayyukan kiyaye muhalli yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China