in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sake yin harbe-harben bindiga a wata makarantar midil dake jihar Californiya ta kasar Amurka
2013-01-11 16:00:46 cri
Bayan harbe-harben bindiga a makarantar firamare ta Sandy Hook da ke kasar Amurka a 'yan kwanakin baya, yadda za a sa kulawa game da mallakar bindiga ya kawo ka-ce-na-ce a zamantakewar al'ummar kasar, yayin da kuma a ranar 10 ga wata da safe, aka sake samun harbe-harben bindiga a wata makarantar midil da ke birnin Taft da ke jihar Californiya.

Bisa rahoton da aka bayar, an ce, a wannan rana da misali karfe 9 da safe, wani mutum da ke dauke da bindiga ya shiga makarantar midil da ke birnin na Taft, sannan kuma ya bude wuta, lamarin da ya jikkata mutane 2.

Yayin da wannan lamari ke tada hankulan al'ummar kasar, shugaban kasar Barack Obama ya nada mataimakinsa Joe Biden don tsara matakan da za a dauka, wajen sa kulawa game da batun mallakar bindigogi a kasar. A ranar 10 ga wata, Biden ya yi shawarwari da mambobin kungiyar bindigogin kasar, wadda ke nuna goyon baya ga mallakar bindiga cikin 'yanci. Bayan shawarwarin, Biden ya jaddada cewa, ko da yake yanzu ba wata hanyar da za a bi wajen hana harbe-harben bindiga, amma lokaci ya yi da za a dauki wani mataki don magance irin wannan lamari. An bayyana cewa, kafin ranar 15 ga wata, Biden zai fitar da wasu matakai don kara sa kulawa game da mallakar bindigogi daga duk fannoni, kuma zai mika su ga shugaban kasar Amurka Barack Obama.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China