in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani hadarin mota ya hallaka mutane 6 a Nigeria
2013-01-09 11:04:39 cri

Wasu mutane 6 da suka hada da maza 2 da mata 4 sun rasa rayukansu, baya ga wasu mutanen 4 da suka samu raunuka, sakamakon wani hadarin mota da ya rutsa da su a kan titin Abuja zuwa Lokoja dake tsakiyar Nigeria a ranar Talatar da ta gabata. Wannan dai hadarin mota ya auku ne a kauyen Karara, bayan da wata karamar motar fasinja ta yi taho-mu-gama da wata karamar safa dake dauke da fasinjoji da dama. Kwamandan rundunar hukumar kare hadurra reshen jihar Kogi Garba Mohammed, ya tabbatar da faruwar wannan lamari, yana mai cewa, tuni aka garzaya da mutane 4 da suka raunana asibiti, yayin da aka kai gawawwakin wadanda suka rasu wajen ajiya dake wani asibiti mallakar jihar.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China