in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya jaddada bukatar raya kasar Sin mai son zaman lafiya da kuma mai zaman doka
2013-01-07 20:16:30 cri
Ranar Litinin 7 ga wata, an yi wani taro kan dokokin shari'a a kasar Sin, inda babban magatakardan kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin, kana shugaban kwamitin soja na tsakiya na JKS Xi Jinping ya yi muhimmin bayani dangane da ayyukan dokokin shari'a da ake gudanarwa a sabon yanayin da ake ciki.

Mista Xi ya ce, ya kamata hukumomin dokokin shari'a na kasar Sin su tafiyar da ayyukansu daidai bisa fatan da al'ummar kasar ke nunawa a fannonin shimfida zaman lafiya, nuna adalci, kiyaye hakkoki da sauransu, a kokarin raya kasar Sin mai son zaman lafiya, kana mai bin doka da oda.

Bugu da kari kuma, Xi Jinping ya bukaci a zurfafa sauye-sauye ga tsarin dokokin shari'a, da kin amincewa da duk wata shari'a da ba adalci a ciki, da kuma yaki da cin hanci da rashawa a fannin dokokin shari'a.

Hakazalika, Mista Xi ya jaddada cewa, ya kamata hukumomin shari'a su yi kokarin gamsar da al'umma game da duk wata shari'ar da suka yi, ta yadda jama'a za su iya ganin adalci da daidaici a ciki.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China