in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
SHIRYE SHIRYE DANGANE DA FARA CIN KOFIN KWALLON KAFAR NA NAHIYAR AFIRKA NA CI GABA DA WAKANA, INDA A YANZU YA RAGE KASA DA MAKWANNI 3 A FARA WANNAN GASA
2013-01-03 16:54:50 cri
Kasashe 16 ne dai ake fatan zasu taka leda yayin gasar cin kofin kwallon kafa na nahiyar ta Afirka a bana, wanda kuma za a fara cikin watan Janairun wannan shekara.

Kasashen Ivory Coast, da Ghana, Cape Verde, Africa ta kudu, da Angola, na cikin wadanda 'yan wasan su zasu baje basirar su yayin gasar. Ragowar kasashen sune Morocco, Niger, Jamhuriyar Demokuradiyyar Congo, da Zambia. Sai kuma Nigeria, da Burkina Faso, da Algeria, Tunisia da Mali da Habasha da kuma Togo. Kamar dai yadda tuni hukumar kwallon kafa ta duniya ta bayyana hakan.

A halin da ake ciki wadannan kungiyoyin kasashe sun riga sun gudanar da wasannin sada zumunta, a wani mataki na share fagen tunkarar kalubalen dake gaban su.

A shekarun baya a kan iya bayyana kasashe mafiya karfi da ka iya lashe wannan gasa, amma a baya bayan nan mawuyacin abu ne kai tsaye a bayyana wasu kasashe kalilan a matsayin zakaru, duba da yadda kasashe daga ko wane fanni na wannan nahiya ta Afirka ke bayyana kwazon su yayin wannan gasa. Ya dai isa misali ganin yadda yayin wannan gasa data gabata, kasar Zambia ya lashe kofin, bayan dauki ba dadi da aka yi tsakanin ta da kasar Ivory Coast. Duk kuwa da manyan 'yan wasa dake taka leda a manyan kulaflikan duniya dake tawagar kungiyar ta Ivory Coast, irin su Didier Drogba, da Kolo Toure, Didier Zokora da dai sauran su.

Ganin yadda wannan gasa ke cigaba da karatowa tuni manazarta harkokin wasan kwallo suka fara furta albarkacin bakin su, tare da hasashen irin kungiyoyin da ka iya yin rawar gani. Cikin tambayoyin da ake yi kuwa akwai shin ko ita kasar Zambia dake rike da kambun wannan gasa zata iya kare shi? Ko kuwa kasar Ivory Coast da ta zo ta biyu za ta yunkuro ta sauya tarihin gasar, musamman ma ganin yadda shekarun manyan 'yan wasanta sun fara ja, ga shi kuma wannan kofi ya kufce daga hannun ta tun a shekara ta 2006. A hannu guda kuma akwai kasar Afirka ta kudu da ke matsayin mai masaukin baki, shin ko wannan kasa tana da wani shiri na ganin ba a zo garinta an fita rawa ba?.

Wadannan dai kadan ne daga irin tambayoyin da masu kallo zasu amsa bayan da aka fara taka leda, kamar dai yadda masu iya magana kan ce, ba a san maci tuwo ba, sai miya ta kare.

Batu filayen wasa kuwa akwai filaye 5 da suka hada da na birnin Johannesburg: Soccer City (94,000 capacity)

Durban: Moses Mabhida Stadium (54,000)

Nelspruit: Mbombela Stadium (41,000)

Port Elizabeth: Nelson Mandela Bay Stadium (48,500)

Rustenburg: Royal Bafokeng Sports Palace (42,000)

Dangane da jadawalin wasannin kuwa, an shirya fara buga kwallo cikin wannan gasa ranar 19 ga watan Janairun nan, kamar dai yadda muka ambata, inda ake sa ran bude gasar da wasa tsakanin kasar Afirka ta kudu da Cape Verde, da kuma wasan Angola da Morocco a ranar farko wato 19 ga wata a filin wasa na Johannesburg. Wannan dai wasa zai zamo na farko a gasar, kuma na farko cikin jerin wasannin rukuni na farko wato rukunin A.

Ragowar wasannin dake tafe suna.

Group A

South Africa v Cape Verde 1600 (agogon Afirka ta Kudu), Angola v Morocco 1900

Jan 23

South Africa v Angola 1500, Morocco v Cape Verde 1800

Jan 27

South Africa v Morocco 1700

At Port Elizabeth

Cape Verde v Angola 1700

Group B

(Port Elizabeth unless noted)

Jan 20

Ghana v DR Congo 1500, Mali v Niger 1800

Jan 24

Ghana v Mali 1500, Niger v DR Congo 1800

Jan 28

Ghana v Niger 1700

At Durban

DR Congo v Mali 1700

Group C

(Nelspruit unless noted)

Jan 21

Zambia v Ethiopia 1500, Nigeria v Burkina Faso 1800

Jan 25

Zambia v Nigeria 1500, Burkina Faso v Ethiopia 1800

Jan 29

Zambia v Burkina Faso 1700

At Rustenburg

Ethiopia v Nigeria 1700

Group D

(Rustenburg unless noted)

Jan 22

Ivory Coast v Togo 1500, Tunisia v Algeria 1800

Jan 26

Ivory Coast v Tunisia 1500, Algeria v Togo 1800

Jan 30

Ivory Coast v Algeria 1700

At Nelspruit

Togo v Tunisia 1700

Quarter-finals

Feb 2

At Port Elizabeth

(1) Gp B winners v Gp A runners-up 1500

At Durban

(2) Gp A winners v Gp B runners-up 1830

Feb 3

At Rustenburg

(3) Gp D winners v Gp C runners-up 1500

At Nelspruit

(4) Gp C winners v Gp D runners-up 1830

Semi-finals

Feb 6

At Durban

Winners quarter-final 2 v winners quarter-final 3 1500

At Nelspruit

Winners quarter-final 4 v winners quarter-final 1 1830

Third place

Feb 9

At Port Elizabeth

Semi-finals losers 1800

Final

Feb 10

At Johannesburg

Semi-finals winners 1800

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China