in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Burtaniya ta bayyana manyan ayyukan G8 na shekarar 2013
2013-01-03 16:47:02 cri
Ran 2 ga watan da muke ciki, firaministan Burtaniya David Cameron ya aike da wasiku ga shugabannin kasashe takwas masu ci gaban masana'antu watau G8, inda ya bayyana cewa, manyan ayyukan dake gaban kungiyar G8 a shekarar bana su ne, a farfado da yanayin tattalin arzikin duniya, da kuma kyautata harkokin cinikayya, tsarin karbar haraji, da kara gudanar da ayyukan gwamnati a bayyane da dai sauransu.

Tun ranar 1 ga watan Janairu na shekarar bana, kasar Burtaniya ta karbi shugabancin kungiyar ta G8 na wannan karo. Cikin wasikunsa, David Cameron ya nuna cewa, a nashi wa'adin aikin, zai mai da hankali kan ayyukan bunkasa tattakin arziki da kuma kara guraban aikin yi, bugu da kari, kasar Burtaniya za ta goyi bayan cinikayya mara shinge, hukunta masu gudun haraji, inganta tsarin gudanar da ayyukan gwamnati a fili, ta yadda za ta iya kafa wani tsarin tattalin arziki da na gwamnati da na zamantakewar al'umma , inda za a yi kome a bayyane domin jama'a su gani.

Bugu da kari, yayin da ake maganar taron kolin G8 da za a yi a yankin Arewacin Ireland ta kasar Burtaniya a watan Yuni mai zuwa, David Cameron ya bayyana cewa, zai mai da hankali kan harkokin da suka shafi cinikayya, haraji, da kuma gudanar da harkokin gwamnati a fili, don haka ya yi kira ga shugabannin G8 da su inganta ayyukan tattalin arziki cikin 'yanci, da gudanar da ayyukan gwamnati a fili da kuma bai wa kamfanonin kasar goyon baya ta yadda za a iya cimma burin bunkasa tattalin arziki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China