Madam Hua ta kara da cewa, kasar Sin ta taimaka wa Afirka wajen gina asibitoci da cibiyoyin yaki da zazzabin cizon sauro, da tura kungiyoyin jiyya zuwa kasashen Afirka, da samar musu magunguna da kayayyakin jiyya, kana da horar da likitocin wurin.
Haka kuma inji Madam Hua, a ko da yaushe kasar Sin ta kan dora muhimmanci kan ingancin magunguna, da yaki da hadawa tare da saida magungunan jabu. Game da batun fitar da magunguna zuwa ketare, kasar Sin ta kan bi ka'idojin kasa da kasa, da samar da takardun shaida ingancin magunguna bisa bukatar hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO, da kuma daukar tsauraran matakai a kan batun da ya shafi magunguna jabu. A waje daya kuma, kasar Sin na fatan ganin 'yan kasuwa na kasashen waje su shigad da kayayyaki daga halaltattun masana'antu.(Kande Gao)