Masana daga kasashen nahiyar Afirka sun gabatar da jerin sunayen 'yan takara a zaben da BBC ya yi. A karshe, Katongo ya samu kuri'u fiye da kashi 40 cikin dari.
A watan Febrairun bana, Katongo ya taimaki kungiyar kasarsa ta Zambia wajen shiga gasar cin kofin Afirka, inda kungiyar sa ta doke kungiyar kasar Cote d'Ivoire da mashahurin dan wasa Didier Drogba ya jagora ta hanyar bugun daga ka sai mai tsaron gida.
A ganin BBC, idan Katongo ya ci gaba da gwada kwarewa a kungiyar kasarsa ta Zambia, karfin kungiyar zai dada inganta zuwa wani sabon matsayi. A kuma gabar da ake hangen karatowar gudanar gasar cin kofin duniya a kasar Brazil cikin shekarar 2014, ana dakon ganin ko Katongo zai ci gaba da jagorantar kungiyar kasar ta Zambia, wajen samun kyakkyawan sakamako. (Zainab)