in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci da a gudanar da bincike kan harbo wani jirgi mai saukar ungulu na sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD a Sudan ta Kudu
2012-12-24 20:37:32 cri
Ranar Litinin 24 ga wata ne, mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Madam Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin bata ji dadi ba ko kadan game da harbo wani jirgin sama mai saukar ungulu na sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD da aka yi a Jamhuriyar Sudan ta Kudu, tana mai mika jajenta ga MDD da kuma ta'aziyarta ga iyalan mamatan.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, bisa kuskure ne sojojin kasar Sudan ta Kudu suka harbo wani jirgin sama mai saukar ungulu na sojojin kiyaye lafiya na MDD, abun da yayi sanadiyyar mutuwar dukkan ma'aikatan jirgin hudu. Sai dai madam Hua ta ce, babu basine a cikin mamatan.

Madam Hua ta kara da cewa, an tattauna wannan lamari a gun kwamitin sulhun MDD, kuma kasar Sin ta nemi bangarori daban-daban da su gaggauta gudanar da bincike kan wannan lamari, da daukar matakan da suka wajaba don kaucema aukuwar irinsa nan gaba, da tabbatar da zaman lafiyar sojoji masu shimfida zaman lafiya.(Murtala)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China