in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta cimma burin harba taurarin dan Adam sau 19 a bana
2012-12-19 16:02:39 cri

A ran 19 ga wata, bisa kididdigar da hukumar masana'antun fasahohin tsaron kasar Sin ta fitar, da misalin karfe 12 da minti 13 na tsakar daren yau Laraba, aka harba tauraron dan Adam na GK-2 mallakar kasar Turkiya zuwa hanyarsa ta sararin samaniya, ta hanyar amfani da injin roka mai daukar tauraron dan Adam na Changzheng lambar 2D. Wannan aiki dai ya gudana ne a cibiyar harba tauraron dan Adam ta Jiuquan dake kasar Sin, kuma kawo wannan lokaci, wannan shi ne karo na 174 da aka yi amfani da injunan roka masu daukar tauraron dan Adam na Changzheng domin harba taurarin dan Adam zuwa sama, don haka kasar Sin ta cimma burin harbar taurarin dan Adam sau 19 da ta tsara gudanarwa a bana.

Turkiya ta kera wannan tauraron dan Adam na GK-2 da kanta, kuma shi ne tauraron dan Adam na biyu da kasar ta kera domin aikin nazarin yanayin kasa. Bugu da kari, ma'anar kammalar wannan aiki ga kasar ta Sin bai tsaya kawai ga nuna muhimmin ci gaba a fagen ayyukan cinikin harba taurarin dan Adam masu bin hanyoyin sararin samaniya da ta samu cikin shekaru 10 ba ne, a hannu guda, wannan ne karon farko da injin roka mai daukar tauraron dan Adam na ChangZheng lamba 2D ya shiga kasuwar harba taurarin dan Adam ta duniya.

Bugu da kari, bisa labarin da aka samu, a shekarar 2013, kasar Sin za ta harba kumbo mai dauke da mutane na Shenzhou lamba 10, da injin binciken wata na Chang'e lamba 3,da kuma wasu taurarin dan Adam kimanin 20 daki daki. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China