in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kiyasta cewa, yawan 'yan gudun hijira na Sham zai karu matuka
2012-12-16 16:45:06 cri
Ranar 15 ga wata, António Guterres, jami'in musamman na MDD mai kula da harkokin 'yan gudun hijira da madam Kristalina Georgieva, mambar kwamitin kungiyar kawancen kasashen Turai EU mai kula da harkokin yin hadin gwiwa a tsakanin kasa da kasa, da ba da agajin jin kai da tinkarar barazana sun bayyana a birnin Beirut, hedkwatar kasar Lebanon cewa, sakamakon tsanancewar matsalar kasar Sham ya sa yawan 'yan gudun hijira da suka gudu zuwa kasashen waje daga Sham zai karu kwarai da gaske.

Yanzu wadannan jami'ai 2 suna nan suna ziyara a Lebanon, inda suka yi shawarwari da Najib Mikati, firaministan kasar. Bangarorin 3 sun ba da muhimmanci kan tattauna halin da ake ciki a fannin tinkarar matsalar Sham, musamman ma matsalar jin kai da 'yan gudun hijira na kasar suke fuskanta da kuma bai wa Lebanon tallafi da dai sauransu.

Jami'an 2 sun nuna cewa, ya kamata kasashen duniya su hada kai da kasashen da suka tsugunar da wadannan 'yan gudun hijira yadda ya kamata, su kuma share fagen tinkarar matsanancin halin da za a fuskanta a nan gaba. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China