in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara jefa kuri'ar raba gardama kan daftarin kundin tsarin mulkin kasar Masar a yau
2012-12-15 16:40:54 cri
An fara jefa kuri'ar raba gardama a zagaye na farko kan daftarin kundin tsarin mulkin kasar Masar a safiyar yau Asabar 15 ga wata a jihohi 10 na kasar, kamar Alkahira, Alexandria, Assiut, Aswan da sauransu. Sojoji da 'yan sandan kasar suna share fage a kokarin tabbatar da gudanar da zaben lami lafiya.

A jiya dai dubu-dubatan mutanen kasar Masar sun mamaye tituna domin nuna kiyayya wassu kuma don nuna goyon baya kan kada kuri'a. Bugu da kari, a wannan rana, an yi taho mu gama tsakanin magoya baya da masu adawa da shugaba Mohamed Morsy a birnin Alexandria dake dab da tekun Bahar Rum.

Sojojin kasar sun shirya sosai domin tabbatar da jefa kuri'ar raba gardama lami lafiya inda kawo yanzu kimanin sojoji dubu 120 da motocin yaki dubu 6, ciki har da tankoki, suna zaman ko ta kwana.

Sai dai yanzu ana damuwa kan wasu harkoki, misali, har yanzu ba a samu isassun alkalai wajen sa ido kan jefa kuri'ar raba gardama. Ko da yake kwamitin yanke shari'a a matsayin matakin koli na kasar Masar ya riga ya amince da alkalai da su shiga wannan aiki, amma wasu alkalai sun nuna kiyayya kan wannan batu. A sakamakon karancin yawan alkalai masu sa ido, dole ne ya sa aka raba aikin kashi biyu, wato bayan da aka kammala jefa kuri'a a ranar 15 ga wata, za a ci gaba da jefa kuri'a a zagaye na biyu a ranar 22 ga wata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China