in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Kongo Kinshasa da masu adawa da ita sun fara shawarwari
2012-12-08 16:29:55 cri
Wasu jami'an gwamnatin jamhuriyar Demokuradiyyar Kongo da wakilan dakarun M23 wadanda ke kin jinin gwamnatin sun isa birnin Kampala, fadar mulkin kasar Uganda, a ranar 7 ga wata, inda suka fara shawarwari don kawo karshen rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa a tsakaninsu.

Kasar Uganda, makwabciyar jamhuriyar Demokuradiyyar Kongo, wadda ke kokarin shiga tsakanin bangarorin kasar, ta ba da labarin cewa, gwamnatin kasar Kongo Kinshasa da dakarun M23 sun fara shawarwari ne a ranar 7 ga wata, batutuwa mafi muhimmanci da za a tattauna a kai, su ne yadda za a tsara wasu muhimman manufofi don gudanar da shawarwari, da wa zai sa ido kan batun shawarwarin.

A wajen taron shawarwarin, wani wakilin dake wakiltar kungiyar al'ummar jama'ar Kongo Kinshasa ya bayyana wa manema labaru cewa, abun da ya fi muhimmanci ga jamhuriyar Demokuradiyyar Kongo shi ne zaman lafiya, don haka dole ne bangarorin 2 dake fada da juna su kwance damara domin gudanar da shawarwari. Wakilin ya kara da cewa, jama'ar kasar suna son zaman lafiya, domin suna fatan gudanar da ayyukansu yadda ya kamata a gidajensu, sa'an nan yaransu su je makarantu ba tare da matsala ba. Ban da haka, ya bayyana niyyarsa ta samar da zaman lafiya da ci gaban al'ummar kasar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China