in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na M.D.D. ya sake tsawaita wa'adin hana shigar da makamai kasar Kongo(kinshasa)
2012-11-29 14:49:40 cri
A jiya Laraba 28 ga wata, kwamitin sulhu na M.D.D ya zartas da wani kuduri, inda aka tsaida kudurin tsawaita wa'adin hana shigar da makamai cikin kasar Kongo(kinshasa) har zuwa ranar 1 ga watan Febrairu na shekarar 2014.

Bisa kudurin da aka cimma, kwamitin sulhu na M.D.D ya bukaci dukkanin kasashen duniya da su toshe dukkan wata kafa da za a iya amfani da ita ta jiragen sama, da na ruwa, don samar, ko sayar, ko kuma musayar makamai da harsashi ga kungiyoyi da jama'a masu zaman kansu da suke aiki a kasar Kongo(kinshasa). A kuma hana ba da shawara da ke da nasaba da koyar da dabarun soja, da ba su kudade ko tallafi da dai sauransu.

Ban da wannan kuma, kudurin ya bukaci 'yan tawayen M23 da sauran kungiyoyin 'yan tada kayar baya da su dakatar da tashe-tashen hankula da su iya kawo cikas ga zaman lafiyar kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China