in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da taron tattaunawa na hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka a Hainan na kasar Sin
2012-11-28 10:58:10 cri
An gudanar da taron tattaunawa karo na uku game da hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka daga ranar 27 zuwa 28 ga wata a birnin Wanning dake lardin Hainan na kasar Sin. A yayin wani taro na musamman da aka shirya a lokacin taron tattauawar, mai bada mashawa na sashen kula da harkokin nahiyar Afirka na ma'aikatar harkokin waje ta kasar Sin Long Ling ya bayyana cewa, za a ci gaba da fadadawa da kuma zurfafa hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka.

Long Ling ya ce, yayin da ake samun bunkasuwar tattalin arziki a kasashen Afirka, za a kara samun dama da kuma fuskantar kalubale kan hadin gwiwa a tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, kana za a fadada wannan hadin gwiwar sannu a hankali. Ya zuwa watan Yuni na bana, yawan jarin da kasar Sin ta zuba a kasashen Afirka ya kai dala biliyan 145. Yawan jarin da Sin ta zuba kai tsaye ya kai dala biliyan 15 na wannan adadi.

An kafa tsarin gudanar da taron hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen Afirka a ranar 10 ga watan Nuwanba na shekarar 2010, inda aka gudanar da karo na farko a nan birnin Beijing. Ana gudanar da taron ne a kowace shekara don inganta aiwatar da ayyukan nan gaba da aka tsara a gun dandalin tattaunawa kan hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka da ake gudanarwa shekaru uku-uku. Wannan taro wani muhimmin dandali ne na yin mu'amala a tsakanin kamfanonin Sin da kasashen Afirka. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China