in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya yi kira da a hana cin zarafin mata
2012-11-24 16:42:55 cri
Ranar Lahadi 25 ga watan Nuwamba ta kasance ranar kasa da kasa ta hana cin zarafin mata. Don haka, babban magatakardan MDD Ban Ki-moon ya yi jawabi a ranar 23 ga wata, inda ya yi kira ga kasashe daban daban da su cika alkawarinsu na hana duk wani irin ayyukan cin zarafin mata, kana ya jaddada cewa, ya kamata, a kau da ra'ayin nuna bambanci wanda ke ba da dama ga nuna karfin tuwo tsakanin al'umma.

Cikin jawabinsa, Mista Ban ya ce, ana kai hari, fyade, da kisan miliyoyin 'yan mata a wurare daban daban na duniya, lamarin da ya kasance masu aikata hakan suna cin karen su babu babbaka wajen keta hakkin bil Adama. Sai dai kuma wadanda suka aikata laifi su kan samu damar tsallake hukunci,sakamakon al'adar kare masu aikata laifi wadda ta sa 'yan mata suke jin tsoron fadin abubuwan da aka yi musu.

A cewar Mista Ban, kungiyar hana cin zarafin mata ta majalisarsa tana kokarin neman janyo hankalin gwamnatocin kasashe daban daban, da kungiyoyin kasa da kasa da na jama'a, kafofin watsa labaru da dai sauransu, domin su ma su shiga wannan aiki. Wani binciken da kungiyar ta yi ya sheda cewa matasa da yawa sun yi kira da a kara mai da hankali kan kare 'yan mata, da yada ra'ayin tabbatar da hakkin bil Adama, gami da hada kan bangarori daban daban domin taimakawa matan da aka ci zarafinsu. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China