in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta yi kira ga sassa daban daban na Congo(Kinshasa) da su warware rikici ta hanyar tattaunawa
2012-11-21 16:26:48 cri
A yau 21 ga wata ne a nan Beijing, Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana cewa, kasar Sin tana sa kulawa sosai kan halin da ake ciki a gabashin kasar Congo(Kinshasa), ta kuma nuna damuwa sosai kan matakan tsaron yankin da lalacewar halin jin kai a wurin.

Madam Hua ta kara da cewa, kasar Sin na fatan sassa daban daban da lamarin ya shafa za su warware rikici ta hanyar yin tattaunawa bisa tushen girmama da tabbatar da ikon mulkin kasa da cikakkun yankunan kasa, ta kuma yi kira ga kasashen duniya da kungiyoyin shiyya-shiyya da su ci gaba da kokarinsu na sassauta al'amura a gabashin Congo(Kinshasa) da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yammaci da tsakiyar shiyyar Afirka. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China