in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya sa lura sosai ga sabbin rikice-rikicen da aka samu a tsakanin Palesdinu da Isra'ila
2012-11-13 10:26:48 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayar da wata sanarwa ta hannun kakakinsa a ranar 12 ga wata, ida ya sa lura sosai ga sabbin rikice-rikicen da aka samu a zirin Gaza da yankin kudancin kasar Isra'ila a kwanakin baya.

Sanarwar ta ce, wadannan rikice-rikice sun haddasa mutuwar Palasdinawa da dama, kana fararen hula da sojoji daga bangarorin biyu wato Palesdinu da Isra'ila da dama sun ji rauni, don haka Ban Ki-moon ya maida hankali sosai kan lamarin.

Ban da wannan kuma, Ban Ki-moon ya sake yin kira ga dakarun Palesdinu dake zirin Gaza da su dakatar da kai hare-hare ga wurare daban daban na kasar Isra'ila ba tare da bata lokaci ba, kana ya yi Allah wadai da hare-haren da aka kai. Hakazalika Ban Ki-moon ya yi kira ga kasar Isra'ila da ta yi hakuri, da kuma yin kira ga bangarorin biyu da su yi kokarin magance tsanantar rikice-rikice a tsakaninsu tare da tabbatar da tsaron lafiyar fararen hula a kasashen biyu.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, dakarun Palesdinu dake zirin Gaza da sojojin kasar Isra'ila sun kabsa a ranar 10 ga wata, lamarin da ya haddasa mutuwar Palesdinawa 5 kana mutane fiye da 40 suka ji rauni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China