in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Masanin OECD ya ce, ci gaban tattalin arzikin kasar Sin na kawo sabon karfi ga kokarin karuwar tattalin arzikin kasa da kasa
2012-11-10 20:25:12 cri
A ran 9 ga wata, Mr. Jose Angel Gurria Trevino, babban sakataren kungiyar hadin gwiwa da ci gaban tattalin arziki ta kasa da kasa, OECD ya ce, tattalin arzikin kasar Sin ya samu farfadowa, kuma yanzu yana ci gaba da dorewa. Hakan zai kawo sabon karfi ga kokarin karuwar tattalin arzikin kasa da kasa.

Mr. Angel Gurria ya fadi haka ne a yayin da yake ganawa da wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua na kasar Sin a hedkwatar OECD dake birnin Paris na kasar Faransa. Ya kuma yi hasashen cewa, tattalin arzikin kasar Sin zai karu tsakanin kashi 7.5 cikin dari da kashi 7.7 cikin dari a bana, sannan zai karu da kashi 8 cikin kashi dari a shekarar 2014, kuma zai ci gaba da samun ci gaba da dorewa cikin shekaru 50 masu zuwa.

Mr. Angel Gurria ya kara da cewa, har yanzu maganar tattalin arziki batu ne da ke jawo hankalin kasa da kasa. Wasu sabbin kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin za su ci gaba da samun bunkasuwa cikin sauri cikin shekaru masu zuwa, kuma mai yiyuwa ne nan da shekaru 50 masu zuwa, za su wuce kasashe mambobin kungiyar OECD, hakan zai canja halin da ake ciki ta fuskar tattalin arzikin kasa da kasa gaba daya. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China