in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin injiniya da kasar Sin za ta tura su zuwa kasar Sudan ta kudu domin na kiyaye zaman lafiya sun yi rantsuwa
2012-11-10 17:04:55 cri
A yau 10 ga wata da safe ne, sojoji da hafsoshi 275 wadanda kasar Sin za ta tura su zuwa yankin Wawu na kasar Sudan ta kudu domin tabbatar da zaman lafiya a yankin suka yi rantsuwa. Wadannan sojojin injiyoyi za su tashi zuwa yankin Wawu a ran 15 ga wata, sannan wani karamin rukunin jinyya dake kunshe da mutane 63 zai isa yankin tare da su.

Nauyin da aka dora wa wadannan sojoji injijniya na kasar Sin shi ne gyara da shimfida hanyoyin mota, gadoji da filin tashi da saukar jiragen sama, tare da gyara injunan samar da ruwan sha da na samar da wutar lantarki, da lalata harsassai da makamai, har ma za su ba da taimako ga sauran rundunonin tabbatar da zaman lafiya a kasar Sudan ta kudu idan akwai bukata. Wa'adin aiki nasu a kasar Sudan ta kudu zai kai tsawon watanni 8. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China