in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jam'iyyoyin siyasa na kasashen kudancin Sahara sun mai da hankali kan babban taron wakilan JKS karo na 18
2012-11-05 15:01:23 cri
Kwanan baya, a yayin wani intabiyu da 'dan jaridar gidan rediyon CRI ya yi masa, wani jami'in ma'aikatar cudanya da kasashen waje ta kwamitin tsakiya na jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin Chao Weidong ya nuna cewa, jam'iyyoyin siyasa da manyan jami'ai na kasashen dake kudu da Sahara sun mai da hankali sosai kan babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18.

Chao Weidong ya nuna cewa, a yayin da yake ganawa da wasu jami'an kasashen Afirka, ya lura cewa, wasu jam'iyyoyin siyasa da manyan jami'ai na kasashen kudancin Sahara sun mai da hankali sosai kan ayyukan shirinmu kan babban taron wakilan jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin karo na 18 kuma suna fatan za a samu nasarori da dama a cikin taron. Kuma wasu jami'an sun nuna cewa, babban taron nan ya zama wani muhimmin taron wanda zai takaita ayyukan kasar na shekaru 10 da suka gabata, har zai taimaka wajen gudanar da ayyukan kasar na gaba, sun kuma yi imani cewa, sabbin shugabannin Sin za su dukufa matuka wajen kara kyautata zaman rayuwar jama'ar Sin.

Chao Weidong ya bayyana cewa, jam'iyyoyin kasashen Afirka suna mai da hankali sosai kan dangantakar da ke tsakaninsu da jam'iyyar kwaminis ta Sin, suna fatan za a yi musaya ra'ayi mai zurfi tsakanin bangarorin biyu, ta yadda za a iya yin cudanya kan fasahohin da aka samu da kuma fuskantar da kalubaloli don cimma burin ci gaba tare.

Ya kuma nuna cewa, ya zuwa yanzu, an riga an samun sakwannin taya murna daga wasu kasashen Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China