in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bada lambar yabo ta wurin yawon shakatawa mafi kyau na nahiyar Afirka ga birnin Marrakech na kasar Morocco
2012-11-04 17:12:44 cri
Bisa labarin da kamfanin dillancin labaru na kasar Morocco ya bayar a ranar 3 ga wata, an ce, kwamitin bada lambobin yabo na wuraren yawon shakatawa mafi kyau na duniya ya gudanar da wani zabe a kwanakin baya, inda aka bada lambar yabo ta wurin yawon shakatawa mafi kyau na nahiyar Afirka na shekarar 2012 ga birnin Marrakech dake kudancin kasar Morocco.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, bayan da masu aikin yawon shakatawa, masana da kuma masu nazari daga kasashe da yankuna 170 suka jefa kuri'u, birnin Marrakech ya doke birnin Cape Town na kasar Afirka ta kudu inda ya zama wurin yawon shakatawa mafi kyau na nahiyar Afirka.

Birnin Marrakech yana daya daga cikin manyan birane 4 da sarakunan kasar Morocco suka zaune a tarihi, wanda ya shahara domin kasancewar mashahuran wuraren shan iska da dama dake wurin, kuma an baiwa kudancin kasar Morocco suna birnin lu'u-lu'u. Kana dukkan gine-ginen dake birnin suna da launin ja, don haka aka kiran birnin da sunan "birni mai launin ja".

Birnin Marrakech ya jawo hankalin masu yawon shakatawa da dama daga kasa da kasa, kana sau shida birnin ya samu lambar yabo ta wurin yawon shakatawa mafi kyau a dandalin yawon shakatawa na duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China