in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta ce an samu karin 'yan Mali 85,000 da suka yi gudun hijira
2012-11-03 19:06:28 cri
Mataimakin kakakin MDD, Eduardo del Buey, ya furta a jiya Jumma'a 2 ga wata cewa, hukuma mai kula da 'yan gudun hijira dake karkashin majalisar ta daidaita jimillar da ta gabatar game da yawan mutanen kasar Mali da suka yi gudun hijira daga gidajensu zuwa wassu wurare dake cikin kasar, jimillar da ta karu daga 118,795 zuwa 203,845, wato ta karu da a kalla mutane 85,000.

A cewar del Buey, jimillar da aka daidaita ta nuna yadda aka samu ci gaba wajen shiga cikin yankin arewacin kasar Mali, gami da yadda ayyuka suka samu gyaruwa a fannin kidayar mutanen da suka yi gudun hijira a Bamako, fadar mulkin kasar.

A watannin da suka gabata, MDD ta sanar da damuwarta wajen gano karin masu tsattsauran ra'ayi a kasar Mali, da cin zarafin mutane, da tsananin talauci da suka yi katutu a kasar. Ban da haka, an ba da rahotanni kan yawan gano fasa kwaurin makamai, da miyagun kwayoyi, har ma fataucin mutane da aka yi a arewacin kasar Mali.

Kakakin MDD ya ce, jimillar da majalisar ta gabatar ta sheda karin mutanen da suka yi gudun hijira sakamakon rashin kwanciyar hankali, da cigaba da cin zarafin jama'a a arewacin kasar Mali, gami da tsoron matakan soja da za'a iya dauka, da karancin abubuwan amfanin yau da kullum da na more rayuwa.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China