in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin firaministan kasar Sin ya jaddada bukatar martaba dokar kasa da kasa da aka shata bayan yakin duniya na biyu
2012-10-23 20:27:44 cri
Yayin da mataimakin firaministan kasar Sin Li Keqiang yake ganawa da tawagar tsofaffin kusoshin kasar Amurka a ranar 23 ga wata a nan birnin Beijing, ya bayyana matsayin kasar Sin kan batun tsibirin Diaoyu, kana ya jaddada cewa, kamata ya yi kasa da kasa su mutunta dokar kasa da kasa da aka shata bayan yakin duniya na biyu.

A wannan rana, Li Keqiang ya gana da tsohon mai bada taimako ga shugaban kasar Amurka mai kula da harkokin tsaron kasa Stephen John Hadley, tsofaffin mataimakan sakatarorin harkokin wajen kasar Amurka biyu James B. Steinberg da Richard Lee Armitage, da kuma tsohon mai bada taimako ga ministan tsaron kasar Amurka Joseph S. Nye. Li Keqiang ya bayyana cewa, shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 40 da aka sake bude kofa ga juna a tsakanin Sin da Amurka. A cikin wadannan shekaru 40, an samu babban ci gaba kan dangantakar kasashen biyu domin kasashen biyu sun fahimci juna, yin hadin gwiwa da kuma warware manyan batutuwa tare. Ana bukatar kasashen biyu da su bi hanyar da ta dace, girmama juna, kara yin hadin gwiwa, daidaita matsalolin dake kasancewa a tsakaninsu da kuma yin mu'amala a tsakanin jama'arsu don inganta dangantakar abokantaka a tsakaninsu da neman hanyar bunkasa sabuwar dangantaka a tsakanin manyan kasashe.

Bangaren kasar Amurka ya amince da ra'ayin Li Keqiang game da raya dangantakar dake tsakaninta da kasar Sin, kana ya bayyana cewa, ko jam'iyyar democrat ko jam'iyyar republican na kasar Amurka dukkansu su nuna goyon baya ga inganta dangantakar dake tsakanin Amurka da Sin. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China