Sanarwar ta ce, tun bayan da aka yi kwaskwarima ga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar Guinea a watan Satumba na bana dake da nauyin shirya zaben majalisar dokokin, jam'iyyun adawa ba su gabatar da sunayen 'yan takararsu bisa lokacin da aka kayyade ba. Idan hukumar zaben ba za ta kammala aikin gyare-gyare a watan Oktoba na bana ba, wannan zai yi tasiri ga gudanar da zaben kai tsaye.
Dadin dadawa, sanarwar ta jaddada cewa, idan jam'iyyun adawa su ki gabatar da sunayen wakilansu, gwamnatin kasar za ta nemi hanyar daidaita batun bisa dokoki, a kokarin sa kaimi ga gudanar da zaben, ta yadda za a kammala yanayin wucin gadi na mulkin kasar Guinea tun da wuri.(Fatima)