in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Nijer ta shiga gasar cin kofin kwallon kafa na kasashen Afirka na shekarar 2013
2012-10-18 15:33:42 cri
A ranar 14 ga wata a Niamey, babban birnin Jamhuriyar Nijar, aka gudanar da zagayen karshe na wasan neman shiga gasar cin kofin kwallon kafa na kasashen Afirka na shekarar 2013, inda 'yan wasan Jamhuriyar Nijer suka kara da na Guinea. A karshe, Nijer ce ta yi galaba kan kasar Guinea da ci biyu da nema, don haka Nijer ta shiga gasar cin kofin kwallon kafa na kasashen Afirka na shekarar 2013.

Wannan ne karo na biyu da Nijer din ta shiga gasar cin kofin kwallon kafa na kasashen Afirka bayan shekarar 2011. Za a gudanar da gasar ce a wannan karo a kasar Afirka ta kudu a shekarar 2013.

A farkon rabin lokaci na wasan da aka yi tsakanin Nijer da Guinea, babu wadda ta jefa kwallo a ragar wata. Bayan an dawo daga hutun rabin lokaci ne, Mohamed Francisco Chikoto da Boubakar Issoufou daga Jamhuriyar Nijer suka zura kwallayen da suka baiwa kasar nasara. A karshe, Nijer ta doke Guinea da ci biyu da nema

A wasan farko da aka yi tsakanin kungiyoyin biyu a kasar Guinea a ranar 9 ga watan Satumba, Nijer ce ta samu nasara da ci daya mai ban haushi. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China