in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu ya yi Allah wadai da harin da aka kai wa sojojin wanzar da zaman lafiya a Darfur
2012-10-04 17:12:37 cri
Kwamitin sulhun MDD ya ba da sanarwa a ranar Laraba 3 ga wata cewa, ya yi Allah wadai da harin da aka kai wa sojojin wanzar da zaman lafiya na rudunar musamman da MDD da kungiyar tarayyar kasashen Afirka suka girke a yankin Darfur na kasar Sudan (UNAMID).

Shugaban kwamitin sulhun na wannan wata, kuma jakadan kasar Guatemalan a MDD, Gert Rosenthal, ya karanta wannan sanarwa ga manema labaru, inda ya ce wasu dakarun da ba a tantance wanene su ba sun yi kwanton bauna ga wasu sojojin rundunar UNAMID wadanda suka yi rangadi a garin El Geneina na jihar West Darfur da ke kasar Sudan a ranar 2 ga wata, lamarin da ya haddasa mutuwar sojoji 'yan Nijeriya 4, tare da raunatar wasu 8, don haka kasashe mambobin kwamitin sulhun sun yi tofin Allah tsine da babbar murya.

Cikin sanarwar, an kara da cewa, kwamitin sulhun ya yi kira ga gwamnatin kasar Sudan da su gagauta aiwatar da bincike kan lamarin, don gurfanar da masu laifin a gaban kotu. Ban da haka kuma, kwamitin ya sake yin bayanin cewa, zai goyi bayan rundunar UNAMID, kana ya yi kira ga bangarori daban daban na kasar Darfur da su hada kai tare da rundunar. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China