in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jirgin sama na farko da ke dauke da maniyyata aikin Haji ya tashi daga Lanzhou na Sin zuwa Makka na Saudiya
2012-09-26 14:12:52 cri
A daidai karfe 9 saura minti 12 na daren ranar jiya Talata 25 ga wata, jirgin saman farko da maniyyata aikin hajin kasar Sin suka yi hayarsa ya tashi daga birnin Lanzhou na lardin Gansu na kasar zuwa Makka a Saudiya.

Mataimakin babban sakataren kungiyar kula da harkokin addinin musulunci na kasar Sin Jin Rubin ya bayyana cewa, a shekarar da ake ciki, gaba daya musulmai dubu 13 da dari 8 na kasar Sin za su tafi Makka domin aikin haji, wannan jirgin saman da ya tashi daga Lanzhou jiya shi ne na farko da aka yi hayarsa a Sin, daga bisani kuma akwai sauran jiragen guda 40 da za su tashi zuwa Makka daga Beijing, Yinchuan, Urumqi, Kunming da dai sauran birane daya bayan daya.

Gwamnatin kasar Sin ta samar da hidima mai inganci ga manityyata aikin haji a fannoni daban daban, ciki har da masu ba da jagoranci, masu kula da harkokin addini, likitoci da kuma masu dafa abinci. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China