in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar AU ta yi Allah wadai da kisan gilla da aka kai wa 'dan majalisar kasar Somalia a Mogadishu
2012-09-24 14:55:17 cri

Wakilin musamman na shugaban kungiyar da AU ta tura wa kasar Somalia da ake kira AMISOM, Boubacar Diarra, ya yi suka kan kisan gilla da a kai wa sabon zababben 'dan majalisar kasar, Mustafa Mohamed Mo'alin a birnin Mogadishu.

An kashe Mo'alin ne a Waaberi dake birnin Mogadishu a Somalia, yayin da yake kan hanyar dawowa daga salla ran Asabar da yamma.

Diarra ya bayyana cewar, 'yan majalisu su ne ke wakiltar mutanen Somalia don haka duk wani hari da aka kai wa 'yan majalisa, hari ne kan jama'ar kasa kuma ba za'a amince da hakan ba. Ya yi kakkausar suka kan harin da aka kaiwa 'dan majalisar kasar Somalia,wanda aka zaba makonni biyu da suka gabata,inda ya bayyana zaben a matsayin ci gaba da ake samu kan yanayin siyasa a kasar.

Ya ci gaba da cewa, kungiyar ta AMISOM za ta ci gaba da yin bakin kokarinta wajen taimakawa dakarun tsaron Somalia don a samu raguwar barazanar hare-hare a birnin na Mogadishu.

Ya ce, bisa la'akari da irin nasara da aka cimma na kawo karshen mulkin wucin gadi, Somalia da su kansu mutanen kasar sun rungumi sabuwar alkiblar siyasa, don haka, ba za'a bar hari irin wannan da ya gurguntar da gaggarumar nasara da aka cimma ba.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China