in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zanga-zanga sun haifar da tarzoma a Guinee
2012-09-23 17:11:46 cri
Tun daga ranar 20 ga wata, jam'iyyar 'yan hamaya ta kasar Guinee ta fara gudanar da zanga-zanga a birnin Conakry, hedkwatar kasar, domin tilasta wa gwamnatin kasar da ta biya bukatarta ta gudanar da zaben majalisa cikin adalci kuma cikin sauri. A ranar 22 ga wata, ko da yake masu goyon bayan 'yan adawa da dama sun ci gaba da zanga-zanga a wasu sassan Conakry, amma kura ta kwanta a birnin.

Ranar 21 ga wata, a lokacin da suke zanga-zanga, wasu matasan da ke goyon bayan 'yan adawa sun ta da rikici tare da wadanda suke goyon bayan jam'iyyar da ke mulkin kasar, lamarin da ya haifar da tarzoma. A daren wannan rana, kuma jami'an tsaron kasar sun bayyana cewa, wani ya mutu sakamakon tarzomar, yayin da wasu 46 suka jikkata, ciki har da 'yan sanda 13. A ranar 22 ga wata, wasu magoya bayan 'yan adawa sun ci gaba da yin zanga-zanga a wasu sassan birnin Conakry, wadanda suka kone tayoyi domin toshe muhimman hanyoyi, daga baya 'yan sanda sun tarwatsa su. Yanzu dai kura ta kwanta a Conakry. A daren ranar 21 ga wata, shugaba Alpha Conde na Guinee ya yi kira ga jama'ar kasar da su yi hakuri, a kokarin kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a kasar. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China