in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Mali zai halarci zaman taron musammun na kwamitin sasantawa da tsaro na kungiyar ECOWAS
2012-09-16 17:00:46 cri
Ministan harkokin waje da dangantakar kasa da kasa na kasar Mali, Tieman Coulibaly zai halarci ayyukan zaman taron musamman na kwamitin sasantawa da tsaro na kungiyar tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS ko CEDEAO a cewar wata sanarwa da aka fitar a ranar Asabar.

Hakazalika sanarwar ta cigaba da cewa mista Coulibaly zai kuma halarci ayyukan zaman taro na 67 na MDD a birnin New York da za'a bude a ranar Talata mai zuwa.

Kafin ya isa birnin New-York, minista Coulibaly, bayan birnin Abidjan na kasar Cote d'Ivoire, zai kuma isa birnin Paris domin habaka dangantakar dake tsakanin kasarsa da kasar Faransa sannan kuma ya wuce zuwa birnin Bruxelles, cibiyar tarayyar Turai in ji wannan sanarwa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China