in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta fara bayar da hasashen yanayin tsibirin Diaoyu a hukunce yau
2012-09-12 10:59:54 cri
Tun daga ranar 11 ga watan, hukumar kula da yanayin saman kasar Sin za ta fara bayar da hasashen yanayi na tsibirin Diaoyu da wurare makwabta da tsibirin a cikin shirin gidan telibijin na kasar Sin, bugu da kari, hukumar kula da tekun kasar Sin za ta bayar da hasashe kan muhallin yankin teku dake kusa da tsibirin Diaoyu a cikin shirin watsa labarai dumi dumi na gidan telibijin na kasar Sin.

Kasar Sin ta mallaki tsibirin Diaoyu da sauran kanana tsibirai karkashin renonsa tun tuni. Kamata ya yi hukumar kula da yanayin saman kasar Sin da hukumar kula da tekun kasar Sin su dauki nauyin aikin bayar da hasashen yanayin wadannan wurare yadda ya kamata, domin yin rigakafin da kaucewa bala'u daga indallahi. Saboda aikin na da muhimmiyar ma'ana wajen ba da tabbaci ga ayyukan kama kifi da tsaron jiragen ruwa tare da kiyaye ikon mallakar teku na kasarmu baki daya.

Kafin wannan, ana ba da hasashen yanayi kawai ne kan muhallin yankin teku na tekun gabas na kasar Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China