Bayan shugaban kasar Alpha Conde ya gana da shi a wannan rana, Louceny Camara ya sanar da yin murabus. A sa'i daya kuma, Louceny Camara ya kira jam'iyyun siyasa daban daban a kasar da su maida moriyar al'umma da kasar a gaban kome, tare da kawar da bambancin ra'ayi da kuma gudanar da zaben majalisar dokokin tun da wuri.
An ba da labari cewa, tun lokacin da kasar ta gudanar da babban zabe a shekarar 2010, jam'iyyar dake mulki da jam'iyyar adawa sun kasa cimma matsaya guda kan matsalar zaben majalisar dokokin kasar, lamarin da ya sa an jinkitar da lokacin yin zaben sau da dama. Jam'iyyar adawa ta bukaci Louceny Camara da ya yi murabus da kuma kafa sabuwar hukumar zabe. Kwanan baya, hukumomin kasar sun tarwatsa zanga-zangar da kungiyoyi masu yin adawa suka yi, daga baya, ministocin 'yan adawa guda biyu dake cikin gwamnati da mambobin dake cikin hukumar zabe guda 7 sun sanar da yin murabus domin kara matsin lamba ga hukumomin kasar.(Amina)