in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin kasar Jordan za ta yi hadin gwiwa tare da hukumomin duniya wajen tinkarar batun zuwan 'yan gudun hijira daga kasar Syria
2012-09-02 17:27:14 cri
A ranar 1 ga wata, ministan kula da harkokin watsa labaru kuma kakakin gwamnatin kasar Jordan Samih Maayatah ya bayyana cewa, an kara samun 'yan gudun hijira daga kasar Syria da suka zo kasar Jordan, wadanda suka kawo matsin lamba ga kasar Jordan a fannonin siyasa, tattalin arziki da zamantakewar al'umma da dai sauransu. Kasar Jordan ta bayyana cewa, za ta yi hadin gwiwa tare da hukumomin duniya wajen tinkarar batun zuwan 'yan gudun hijira.

A gun taron manema labaru da aka gudanar a wannnan rana, Maayatah ya bayyana cewa, kasar Jordan tana yin kokarin karba da tsugunar da 'yan gudun hijira daga kasar Syria, a halin yanzu, tana fuskantar da hali mai wuya.

Yayin da firaministan kasar Jordan Fayez Tarawneh yake ganawa da wakilin hukumar kula da harkokin 'yan gudun hijira ta MDD a wannan rana, ya nuna cewa, gwamnatin kasar Jordan za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da hukumomin duniya dake da alaka da harkokin 'yan gudun hijira wajen tinkarar batun zuwan 'yan gudun hijira. Kana yana fatan za a kara samun taimako daga kasa da kasa.

Wakilin hukumar kula da harkokin 'yan gudun hijira ya nuna girmamawa da yabo ga kasar Jordan da take karba da tsugunar da 'yan gudun hijira daga kasar Syria, kana ya ce, hukumarsa za ta gudanar da wasu ayyuka bisa tushen girmama ikon mallakar kasar Jordan.

Bisa kididdigar da aka yi, yawan 'yan gudun hijira daga kasar Syria dake kasar Jordan a yanzu ya kai fiye da dubu 177, kana kimanin 'yan gudun hijira fiye da 1500 daga kasar Syria suke shiga kasar Jordan a kowace rana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China