in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin da Benin sun sanya hannu kan wasu yarjeniyoyin tattalin arziki da na fasaha
2012-08-22 11:07:15 cri
Jakadan kasar Sin dake kasar Benin, Tao Weiguang tare da ministan harkokin waje da dunkulewar Afrika na kasar Benin, Nassirou Arifari Bako sun rattaba hannu a ranar Talata a birnin Cotonou kan wasu yarjeniyoyi biyu da suka shafi tattalin arziki da fasaha tsakanin gwamnatocin kasashen biyu.

Bisa tsarin wadannan yarjeniyoyi biyu, gaba daya jimillar kudin da gwamnatin kasar Sin ta baiwa kasar Benin ta cimma kudin Sefa biliyan 16.08 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 30.3 kuma kudaden sun hada da taimakon kudin kyauta kimanin Sefa biliyan 5 kwatankwacin dalar Amuka miliyan 9.5 da kuma wani bashin da babu ruwa na Sefa biliyan 11 kimanin dalar Amurka miliyan 20.6.

Wadannan yarjeniyoyi guda biyu da aka sanya wa hannu sun kasance daya daga cikin ayyukan da aka cimma dake aiwatar bisa ga niyyar da bangaren kasar Sin ya dauka da kuma bisa sakamakon shawarwari tsakanin shugabannin kasashen biyu in ji mista Tao.

Hakazalika ya bayyana batutuwan tsarin gina rijiyoyi 100 domin samar da ruwan sha, gina makarantar koyar da fasahohi da maganar sake gina hanyar mota daga Akassato zuwa Bohicon da gwamnatin kasar Sin ta dauki nauyin zuba kudin ginawa, kuma za a fara wadannan ayyuka kafin karshen wannan shekara. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China