in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu sakamakon bala'in girgizar kasa a Iran ya kai a kalla 250
2012-08-12 20:47:45 cri
Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Iran suka bayar, an ce, yawan mutanen da suka mutu sakamakon bala'in girgizar kasa da karfinsa ya kai 6.2 bisa ma'aunin Richter da ya faru a lardin Azarbaijan na gabas dake arewa maso yammacin kasar Iran a ran 11 ga wata ya kai a kalla 250, yayin da kimanin dubu 2 suka jikkata, har yanzu kuma ana nuna cewa, mai yiyuwa ne yawan mutanen da suka mutu sakamakon wannan bala'in zai karu.

Bisa labarin da aka bayar, an ce, yawancin matattun an same su ne a yankunan karkara. Wannan bala'in girgizar kasa ya ruguza kauyuka kimanin 60 na yankin.

Kana kungiyar jin kai ta Crescent da Red Cross ta Iran ta bayyana cewa, yanzu ta mayar da wani dakin wasannin motsa jiki a matsayin dakin samar da kayayyakin jin kai, inda ta riga ta karbi mutanen da wannan bala'i ya nutsa da su kimanin dubu 16, kuma ta samar da tantuna dubu 3 tare da sauran dimbin kayayyakin jin kai.

Bayan aukuwar bala'in, shugaba Ahmedinejad na kasar Iran ya fitar da wata sanarwa, inda ya nuna ta'aziyya ga wadanda suka mutu sakamakon bala'in, kuma ya nuna jejeto ga wadanda suke fama da bala'in, kana ya bukaci hukumomin gwamnatin kasarsa da su yi namijin kokari na tallafawa wadanda suke fama da bala'in. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China