in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka mutu sakamakon bala'in girgizar kasa a Iran ya karu zuwa 180
2012-08-12 16:53:38 cri
Bisa labarin da kafofin watsa labaru na kasar Iran suka bayar, an ce, yawan mutanen da suka mutu sakamakon bala'in girgizar kasa da karfinsa ya kai 6.2 bisa ma'aunin Richter kuma ya faru a lardin Azarbaijan na gabas dake arewa maso yammacin kasar Iran a ran 11 ga wata ya karu zuwa 180, yayin da kimanin dubu 1 da dari 4 suka jikkata, amma an yi kiyasin cewa, mai yiyuwa ne yawan mutanen da suka mutu sakamakon wannan bala'in zai karu.

Gidan talibijin na kasar Iran ya labarta cewa, girgizar kasa ta ruguza kauyuka guda 4 baki daya, tare da lalata wasu kauyuka guda 6. Wani jami'in dake kula da harkokin samar da kayayyakin jin kai na Iran ya ce, bala'in ya katse dukkan hanyoyin sadarwa da na wutar lantarki a yankin. Don haka, ana amfani da rediyo kawai a kokarin tuntubar hukumomin yankin.

Bugu da kari, hanyoyin samar da ruwan sha sun katse sakamakon bala'in, yanzu ana bukatar ruwan sha, burodi, tantuna da dai sauran kayayyakin zaman rayuwa na yau da kullum. Sannan jami'an wurin sun bukaci mazauna wurin da su kwana a waje don magance sake samun rauni sakamakon aukuwar kananan bala'un girgizar kasa masu tsanani. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China