in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan kasar Aljeriya dake kula da harkokin maghreb zai kai ziyara kasar Nijar
2012-08-05 16:18:03 cri
Ministan kasar Aljeriya dake kula da harkokin magrheb da Afrika, Abdelkader Messahel, zai halarci a ranar Litinin a birnin Niamey na kasar Nijar wani zaman taro na ministocin kasashen wannan yanki domin tattaunawa kan rikicin kasar Mali, in ji wata sanarwar ministocin harkokin waje da kamfanin dillancin labarai na APS ya rawaito.

Baya ga haka, taron zai maida hankali kan matsalar tsaro dake adabar yankin Sahel, musammun ma game da yaki da ta'addanci da aikata laifuffukan kasa da kasa, kamar yadda tarurukan hadin gwiwa da mu'amala na UFL da kwamitin hadin gwiwa na hafsoshin sojojin na CEMOC suka yi.

A cikin jawabinsa a taron kwamitin hafsoshin rundunar sojojin kasashen mambobin CEMOC, da ya gudana ranakun 10 da 11 ga watan Yuli a birnin Nouachoutt na kasar Mauritaniya, babban janar na sojojin kasar Aljeriya, Ahmed Gaid Salah yayi Allah wadai da al'amuran tashin hankali da rikicin kasar Mali ya janyo bisa matsalar tsaro a wannan shiyya, tare da jaddada cewa ya zama wajibi a daidaita wadannan matsaloli cikin gajeren lokaci ta yadda 'yan kasar Mali za su maido da zaman lafiya da tsarin dimokuradiya. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China